A ranar 23 ga wata, an gudanar da taron tattaunawar bunƙasuwar Tibet ta Sin ta 2023 a babban ɗakin taron Beijing. Taken taron shi ne “Sabon yanayi, sabuwar Tibet, da sabuwar tafiya: Sabon babin kiyaye hakkin ɗan Adam da samun bunƙasuwa mai inganci na Tibet”. Ofishin kula da yada labaru na majalisar gudanarwar Sin da gwamnatin Tibet mai cin gashin kanta suka shirya tare, kuma BFSU ta ɗa...
A ranar 4 ga watan Mayu, jakadan ƙasar Haɗaɗɗiyar Ɗaular Larabawa H.E. Ali Obaid Al Dhaheri ya ziyarci BFSU, kuma babban sakataren kwamitin jam’iyyar kwaminisancin jami’ar BFSU Wang Dinghua ya gana da shi.Ɓangarorin biyu sun yi mu’amala game da ƙara haɗin gwiwa a wajen mu’amalar ɗalibai da ziyarar malamai, da horar da ɗalibai da mu’amalar ilmi a tsakaninsu. Bayan ganawa, Dhaher...
Daga ranar 16 zuwa ranar 23 ga watan Afrilu, mataimakin sakataren kwamintin jam’iyyar kwaminisancin jami’ar BFSU kuma mataimakin shugaban jami’ar Jia Wenjian ya ziyarci ƙasashen Czech da Italiya, inda ya ziyarci jami’ar Palacký don tattauna haɗin gwiwa wajen kafa kwalejin Confucius, kuma ya ziyarci kwalejin nazarin kasuwancin Moravian don tattauna haɗin gwiwa a tsakaninsu. Haka kuma, y...
A ranar 9 ga watan Afrilu, a cibiyar nazarin ilmin Tibet ta Beijing, aka fitar da sabon ƙamus na nazarin zamantakewa da kimiyya da fasaha na Sinanci da Turanci da harshen Tibet, kuma BFSU da kamfanin ɗab’in CP sun shirya biki tare.Babban ƙamus na nazarin kimiyya da fasaha da zamantakewa na harsunan Sinanci da Turanci da harshen Tibet da shugaban BFSU kuma mataimakin sakatare janar na kwam...
A ranar 3 ga watan Afrilu, manzon musamman kan batun Sin na shugaban ƙungiyar ba da agaji ta Red Cross kuma direktan sashen gabashin Asiya Pierre Krähenbühl ya shugabanci tawaga don ziyarar BFSU. Shugaban BFSU kuma mataimakin sakataren kwamitin jam’iyyar kwaminisancin jami’ar Yang Dan ya gana da shi.Ɓangarorin biyu sun yi mu’amala game da inganta haɗin gwiwa wajen samar da ayyukan yi da...
A ranar 31 ga watan Maris, shugabar jami’ar Queensland ta Australiya Deborah Terry ta shugabanci tawaga don ziyartar BFSU. Shugaban BFSU kuma zaunannen kwamitin jam’iyyar kwaminisancin jami’ar BFSU Yang Dan ya gana da shi, inda suka daddale yarjejeniyar fahimtar juna ta haɗin gwiwa a tsakanin jami’o’i biyu
A ranar 23 ga watan Maris, shugaban jami’ar Belarusian Anderi Karol ya shugabanci tawaga don ziyartar BFSU. Shugaban BFSU kuma zaunannen kwamitin jam’iyyar kwaminisancin jami’ar BFSU Yang Dan ya gana da shi, inda suka daddale yarjejeniyar musayar ɗalibai a tsakaninsu
A ranar 20 ga watan Maris, an ƙaddamar da bikin murnar ranar Faransanci a faɗar ofishin jakadancin Faransa da ke ƙasar Sin. Ma’aikatar ilmi ta ƙasar Faransa ta karrama shugabar kwalejin nazarin harshe da al’adun Faransancin BFSU Dai Dongmei lambar yabo ta nazari, don jinjina ƙoƙarin da ta yi wajen koyar da harshe da yawaita al’adun ƙasashe masu amfani da harshen Faransanci. Jakadan...
A ranar 20 ga watan Maris, jakadan ƙasar Kazakhstan a ƙasar Sin Shakhrat Nuryshev ya ziyarci BFSU, inda ya halarci bikin buɗe gasar harshen Kazakh karo na farko tsakanin ɗalibai masu koyon harsunan waje na ƙasar Sin. Sakataren kwamitin jami’iyyar kwaminisancin jami’ar Wang Dinghua ya gana da shi, inda suka tattauna batun fara ɗarasin tafinta da bayar da kyautar kuɗin karatu